Dalilin da yasa Sarkin Kano da Gwamna El-Rufai suka tafi kasar Afirka ta kudu


Legit Hausa

Gwamnan jahar Ekiti, ya bayyana dalilin zuwansa kasar Afirka ta kudu yayin da ake samun tashin tashinan hare haren kin baki bakaken fata a kasar wanda hakan yayi dalilin mutuwar bakaken fata da dama, tare da asarar dukiya mai yawa.

Jaridar Premium Times ta ruwaito Fayemi ya bayyana cewa ba wai ya je Afirka ta kudu da nufin halartar taron tattalin arziki na duniya wanda Najeriya ta janye daga zuwa bane, a’a, yace ya tafi kasar ne don halartar taron Stellensbosch wanda wani dan jaridar Najeriya, Dele Ollojede ya gayyaceshi ne.

Haka zalika majiyar Legit.ng ta ruwaito mai martaba Sarkin Kano, Muhammadu Sunusi tare da gwamnan jahar Kaduna Malam Nasir Ahmad El-Rufai duk sun halarci wannan taro na Stellensbosch ne ba wai taron tattalin arzikin ba.

Yan Najeriya da dama sun bayyana bacin ransu biyo bayan watsuwar hotunan mutanen 3 a kasar Afirka ta kudu, a daidai lokacin da gwamnatin Buhari ta yi ma jakadan kasarta kiranye daga Afirka ta kudu bisa rikicin daya kaure, don haka suke ganin ya kamata su ma su ma su dakatar da duk abinda suka je yi a kasar don nuna ba’a tare.

Fayemi ta bakin kaakakinsa Olayinka Oyebode ya bayyana cewa Dele Olojede ne ya gayyaceshi don halartar taron kirkire kirkiren fasaha ta duniya, kuma ya gudana ne a wani yanki dake na tazara sosai daga Cape Town inda ake taron tattalin arzikin kasa. “Babban abin ma shi ne an kammala taron tun kafin gwamnatin ta sanar da janyewa daga taron tattalin arziki na duniya.” In ji shi.
 

DAGA ISYAKU.COM

Latsa Shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp

https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN