Legit Hausa
Bayan kwashe akalla sa'o'i takwas ana zaman kotu kan
shari'ar dake tsakanin shugaba Muhammadu Buhari na APC da Atiku Abubakar na
PDP, shugaban kwamitin Alkalan kotun, Mohammed Garba, ya yi watsi da karar da
PDP da Atiku suka shigar. Kotun zabe ta yanke hukuncin cewa shugaba Muhammadu
Buhari ya cancanci yin takaran kujeran shugaban kasa saboda yana da kwalin
karatun da ake bukata har fiye da haka.
Kotun zaben shugaban kasa ta yi watsi da zargin cewa dan
takaran kujeran shugaban kasa karkashin jam'iyyar Peoples Democratic Party
(PDP), Atiku Abubakar, ba haifaffan dan Najeriya bane kuma bai cancanci takaran
zabe. Kotun ta yi watsi da ikirarin jam'iyyar PDP da Atiku cewa shugaba
Muhammadu Buhari ya yi amfani da yan sanda da sauran jami'an tsaro wajen
magudin zabe. Kotun ta ce akwai tafka da warwara saboda ta yaya PDP da Atiku za
suce jami'an tsaro sun yi magudi kuma su manta da su lokacin shigar da kara
kotu.
Alkalin kotun ya soke dukkan bukatar da hukumar gudanar da
zabe ta kasa mai zaman kanta INEC ta gabatar na watsi da karar jam'iyyar PDP da
Atiku Abubakar. Hukumar INEC ta bukaci kotun zaben ta yi watsi da karar PDP
saboda daya daga cikin lauyoyinta, Dakta Livy, ba sahihin lauya bane.
Hakazalika INEC ta bukaci kotu ta soke bukatar PDP da Atiku na cewa shugaba Buhari
bai cancanci yin takara a zabe ba. Misalin karfe 30, Alkalan kotun zaben
shugaban kasa karkashin jagorancin Alkali Garba Muhammad, sun zauna kuma komai
ya kankama.
Shugaban jam'iyyar APC, Adams Oshiomole; ministan ayyuka da
gidaje, Babatunde Raji Fashola, Shugaban ma'aikatan fadar shugaban kasa, Abba
Kyari, ministan kwadago, Cris Ngige; tsohon gwamnan jihar Bauchi, Mohammed
Abubakar, sun isa kotun. Shugaban jam'iyyar PDP, Uche Secondus, lauyoyin
jam'iyyar PDP, Dakta Livy, Mike Ozekome, sun isa kotu.
Daga cikin wadanda ke kotun akwai, gwamnan jihar Plateau,
Simon Lalong; gwamnan jihar Kebbi, Atiku Bagudu; tsohon shugaban EFCC, Nuhu
Ribadu. Kawo yanzu, lauyoyi biyu sun isa kotun; Cif Charles Edosomwan na
jam'iyyar APC, da kuma Sam Ologunoria na hukumar INEC. Rana ba ta karya, sai
dai uwar da taji kunya - Allah ya kawo mu ranar 178 bayan kammala zaben
shugaban kasa a ranar 23 ga Febrairu, 2019 inda hukumar gudanar da zabe ta kasa
mai zaman ta INEC ta alanta shugaba Muhammadu Buhari matsayin wanda ya lashe
zaben.
Bayan sanar da sakamakon zaben, jam'iyyar PDP da HDP sun
shigar da kara kotun zaben shugaban kasa domin kalubalantar wannan sakamako.
Daga baya, jam'iyyar HDP da dan takararta suka janye kararsu daga kotun bisa
wasu dalilai, amma PDP ta ce sam sai ta ga abinda ya kwancewa kura zani.
DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN