Legit Hausa
Kungiyan yan uwa Musulmai na Shi’a wato Islamic Movement in
Nigeria (IMN) ta shigar da kara domin kalubalantar hukuncin haramta ayyukan
kungiyar da gwamnatin tarayya tayi.
A cikin karar, kungiyar Shi’a ta bukaci kotu da ta janye
umurnin da aka yi a ranar 26 ga watan Yuli na bayyana kungiyar IMN a matsayin
kungiyar yan ta’adda.
Idan za ku tuna gwamnatin tarayyar Najeriya ta sanar da
haramta ayyukan kungiyar Shi’a a karkashin jagorancin Sheikh Ibraheem
El-zakzaky. Mohammed Adamu, sufeto janar na yan sanda, ya sanar da hakan a wani
taron manema labarai a Abuja a ranar Talata, 30 ga watan Yuli.
Wata kotun tarayya da ke Abuja ta kaddamar da kungiyar a
matsayin kungiyar ta’addanci, biyo bayan wani kara da gwamnatin tarayya ta
shigar.
A baya Legit.ng ta rahoto cewa kungiyar da ke kare hakkin
Musulmi (MURIC) a ranar Litinin, 29 ga watan Yuli ta mara wa Gwamnatin Tarayya
baya akan haramta ayyukan kungiyar Islamic Movement in Nigeria (IMN) wanda aka
fi sani da Shi’a da kuma kaddamar da ita a matsayin kungiyar ta’adda.
MURIC ta bayyana matakin a matsayin kudurin da zai karfafa
zaman lafiya da kwanciyar hankali a Najeriya.
DAGA ISYAKU.COM
Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi