Legit Hausa
DAGA ISYAKU.COM
Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Fiye da y’ay’an jam’iyyar APC 12, 562 ne suka yi wankan
tsarki suka tunjuma cikin jam’iyyar PDP, kuma suka samu kyakkyawar tarba daga
gwamnan jahar Zamfara, Gwamna Bello Matawalle. Gwamnan ya karbi dubun dubatan
yayan jam’iyyar ne a ranar Alhamis, 15 ga watan Agusta a garin Gusau, wanda
daga cikinsu akwai tsofaffin kwamishinoni guda uku da suka hada da Alhaji Idris
Keta, Alhaji Abdulkadir Ahmed da Alhaji Aliyu Tsafe.
Majiyar Legit.ng ta ruwaito sauran sun hada da tsofaffin
shuwagabannin kananan hukumomi da suka hada da Alhaji Musa Tsafe da Alhaji
Ahmed Kantoma, da wasu tsofaffin manyan daraktoci Alhaji Bashir Kwaren Ganuwa
da Alhaji Saminu Lawali. Da suke gabatar da jawabansu, Alhaji Idris Keta da ALhaji
Habibu Alo sun bayyana cewa abin da ya ja hankalinsu zuwa jam’iyyar PDP shi ne
zaman lafiyar da ake samu a jahar Zamfara a mulkin Matawalle bayan tsawon
lokaci ana fama da matsalar tsaro.
Manyan yan siyasan biyu sun bayyana cewa shawo kan matsalar
da gwamnan ya yi yasa ya samu aminci daga jama’an jahar, don haka su ma zasu
bashi goyon baya don cigaba da tabbatar da tsaro a kasar. Da yake nasa jawabin,
Matawalle ya bayyana cewa yan siyasa sun yanke hukuncin daya kamata da shigowa
jam’iyyar PDP, kuma ya basu tabbacin ba zai nuna bambanci tsakaninsu da
tsofaffin yan jam’iyyar ba.
Haka nan gwamnan ya tabbatar da cigaba da kokarinsa na
tabbatar da tsaro a jahar Zamfara, tare da inganta rayuwar mutanen da hare
haren yan bindiga ya shafa, sa’annan yace gwamnati za ta samar da wani tsari na
kulawa da yan gudun hijira. Daga karshe gwamnan ya bayyana cewa sun samu goyon
bayan shugaban kasa Muhammadu Buhari tare da taimakonsa don mayar da yan gudun
hijiran zuwa gidajensu nan bada jimawa ba.
DAGA ISYAKU.COM
Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi