Legit Hausa
Jagoran kungiyar Izala ta Najeriya JIBWIS (Jama'atu Izalatul
Bid'ah Wa Ikamatis Sunna), Sheikh Abdullahi Bala Lau, ya shawarci gwamnatin
Najeriya da cewar ya kamata ta yiwa jagoran 'yan shi'a Sheikh Ibrahim Zakzaky
adalci.
Shawarar babban malamin addinin na Islama ta zo ne a yayin
da yake gabatar da hudubarsa ta Juma'a a masallacin babbar cibiyar kungiyar
JIBWIS da ke Utaku cikin birnin Abuja a ranar Juma'a 2 ga watan Agusta. Kamar
yadda jaridar BBC Hausa ta ruwaito, wannan ba shi ne karo na farko ba da wani
babban malamin addinin Sunnah a kasar ya sa baki game da sha'anin jagoran 'yan
shi'a da ke tsare a hannun gwamnati tun a shekarar 2015.
Sheika Bala Lau ya ce: "Babu wanda ba ya son a yi wa
shugabansu (Zakzaky) adalci. Ko kafiri ne a yi wa adalci. Idan abin da ya yi ba
daidai ba ne a hukunta shi saboda gani ga wane, ya isa wane tsoron Allah."
"Idan ba a yi masa hukunci ba zanga-zanga da tawaye za su sa a sake shi.
Idan kuwa aka sake shi to ranar da duk aka kama wani shugaba na kowane addini
mabiyansa su ma su fito su yi zanga-zanga, su yi abin da suka ga dama domin a
saki shugabansu.
"Daga nan babu sauran zaman lafiya kenan," a cewar
sa. Kazalika, ya ce "idan jagoran 'yan Shi'an bai yi laifi ba, to a sake
shi. Idan ko ya yi laifi a yi masa hukunci kamar yadda ake yi wa kowane dan
kasa mai laifi. "Idan aka yi haka an zauna lafiya." Ya ce:
"Akwai wasu da suke kokarin yin amfani da matsalar wajen hada 'yan Izala
fada da 'yan Darika a Najeriya. Suna cewa idan aka gama da 'yan Shi'a su za a
koma wa." Shehin malamin ya kuma kara da cewa yadda wasu ke kokarin
siyasantar da batun jagoran na shi'a ya na ci masa tuwo a kwarya.
DAGA ISYAKU.COM
Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi