Legit Hausa
Wani matashin saurayi da hatsarin mota ya ritsa dashi a
Ikorodu dake jihar Legas ya bayyana cewa mutanen da suka je domin su taimakesu
sun sace mishi kudin dake cikin aljihunshi.
A yadda rahoton ya nuna, hatsarin ya faru ne yayin da tayar
mota ta cire taje ta bige wani mutumi a lokacin da yake tafiya akan babur.
Wannan dalili ne yasa mutane suka yi dafifi domin su dauke
daga kan babbar hanyar wacce motoci ke faman kai kawo, amma kuma a yayin da
mutanen ke kokarin dauke mutumin, wani da ba a san ko waye ba ya sanya hannunsa
a cikin aljihunshi ya dauke mishi kudi kimaninm naira dubu takwas.
Wannan lamari dai bai yiwa mutumin dadi ba, domin kuwa duk
da irin ciwon da yaji bai sa barawon ya tausaya masa ba, ya sakaya hannu ya
zare masa dan kudin da yake riritawa.
Wannan abu da ya faru ba shine na farko ba, saboda ya sha
faruwa a lokuta da dama idan hatsari makamancin haka ya faru a kasar nan.
DAGA ISYAKU.COM
Latsa Shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN