Legit Hausa
Shugaban kungiyar Islamic Movement in Nigeria (IMN), wacce
aka fi sani da Shi’a, Sheikh Ibrahim El-Zakzaky, na a hanyarsa na dawowa
Najeriya daga asibitin Indiya inda ya je yin magani. Kakakin kungiyar ta IMN,
Ibrahim Musa, ya tabbatar wa manema labarai cewa shugaban na Shi’a zai dawo
Abuja da karfe 5:00 na yamma.
Har ila yau, a cewar wani rubutu da aka wallafa a shafin
Twitter daga ofishin Zakzaky, ana sanya ran shugaban kungiyar na IMN zai iso
Abuja da karfe 17:00. Wani bidiyo da aka wallafa tare a shafin Twitter ya kuma
nuno El-Zakzaky yana bayanin cewa asibitin Indiya ta amince za ta bari ya dawo
Najeriya tare da matarsa Zeenat, biyo bayan rikicin da ya barke kan zabi na
likitocin da za su kula da su da kuma ka’idojin jinyan.
Malamin ya bayyana cewa mahukuntan yankin da ya je neman
magani a Indiya sun gaya masa cewa sun yanke hukuncin mayar da shi Najeriya.
Idan za ku tuna dai tun bayan isarsa kasar ta Indiya a ranar Talata aka samu
kiki-kaka kan likitocin da za su duba shi da mai dakinsa, inda ya yi zargin
cewa "an sauya masa likitocin da ya zaba tun farko, yana mai cewa ana
tsare da shi cikin mummunan yanayi".
Sai dai gwamnatin Najeriya ta musanta kalaman nasa, tana mai
cewa ya yi kokarin bijirewa sharudan da kotu ta gindaya masa, sannan ta bai wa
gwamnatin Indiya hakuri kan mummunar halayyar da ya nuna.
DAGA ISYAKU.COM
Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi