Wadansu jama'a a birnin Enugu sun gudanar da zanga zanga bayan an gano gawar wata mata mai dauke da juna biyu an kasheta kuma aka cire jariri da yake cikinta a Nchatancha Nike da ke Enugu ta gabas.
Ana zargin cewa wasu makiyaya ne suka kashe matan, sakamakon haka matasan yankin suka datse babban hanyar Enugu zuwa Abakaliki domin nina fushinsu.
Ita dai matar an ce tana dawowa ne daga gona lokacin da wannan tsautsayi ya rutsa da ita a hannun makiyayan.
DAGA ISYAKU.COM
Latsa Shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN
Shiga seniorapost.com domin saamun labaran turanci