Legit Hausa
Mun samu cewa a ranar Asabar wasu masu yi wa kasa hidima
shida na boge sun shiga hannu a sansanin masu bautar kasa NYSC da ke jihar
Katsina kwanaki kadan bayan da aka fara zaman sansanin na makonni uku. Kamar
yadda jaridar The Nation ta ruwaito, shugaban hukumar NYSC na jihar, Alhaji
Ahidjo Yahaya, shi ne ya bayar da shaidar hakan a wata hira da manema labarai
yayin gabatar da wasu 'yan bautar kasa biyu mata na bogi da aka cafke.
Biyo bayan wani bincike da babban shugaban hukumar NYSC na
kasa, Birgediya Janar Shu'aibu Ibrahim ya jagoranta, an samu nasarar cafke 'yan
bautar biyu da takardun kammala karatun digiri na boge, wanda suka amsa
laifinsu babu wata-wata inji Alhaji Yahaya.
Masu bautar kasar biyu na boge da aka gabatar wa manema
labarai sun bayar da sunayensu tare da lambobin shaida kamar haka: Merienwa
Chimdinma Ngozi (KT/19B/3836) - NYSC /ISU/2019/259331 daga jami'ar jihar Imo da
kuma Offor Chinelo Blessing (KT/19B/3696) - NYSC /ISU/2019/260/22. Ana iya tuna
cewa hukumar NYSC gabanin fara zaman sansanin wadanda suka kammala karatu a
bana, ta yi gargadin cewa ba za ta sassauta wa duk wanda ta damka da takardun
boge, lamarin da ta ce za ta mika shi ga hukumar 'yan sanda domin daukar
mataki.
A wani rahoto mai nasaba da wannan da jaridar Legit.ng ta
ruwaito, tsohuwar ministar kudi ta Najeriya, Kemi Adeosun, ta yi murabus daga
kujerarta bayan an gano laifi da aikata na amfani da takardar shaidar hidimar
kasa ta boge domin samun damar yin aiki a Najeriya.
DAGA ISYAKU.COM
Latsa Shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN