Yanzu Yanzu: Yan Shi’a da ke zanga-zanga sun harbi yan sanda 3 a majalisar dokoki

Legit Hausa
Rahotanni da ke zuwa mana sun nuna cewa mambobin kungiyar Shi’a sun harbi wasu jami’an yan sanda da ke bakin aiki a majalisar dokokin kasar.
Lamarin ya haddasa tashin hankali a cikin harabar majalisar.
Jaridar Premium Times ta ruwaito cewa anyi gaggawan daukar daya daga cikin jami’an yan sandan zuwa asibitin majalisar dokokin da miusalin karfe 1:55 na rana.
Idon shaida da dama da ke wajen, sun bayyana cewa lamarin ya afku ne a lokacin da masu zanga-zangar suka yi kokarin kutsa kai cikin majalisar ta karfin tuwo.
“Sun harbi jami’an yan sanda uku. Daya daga cikinsu ma kamar ya mutu,” inji wani idon shaida.
A daidai lokacin kawo wannan rahoton, jami’an yan sanda sun rufe mashigin majalisar dokokin yayinda karan harbi a sama ya karade ko ina.
DAGA ISYAKU.COM Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN