Legit Hausa
Jami’an rundunar Yansandan Najeriya sun yi fama da mabiya
mazahabar Shia a yayin da suka gudanar da wani gangamin zanga zanga a babban
birnin tarayya Abuja, wanda har ta kai ga sun yi amfani da barkonon tsohuwa.
Jaridar Sahara Reporters ta ruwaito yan shia’an suna gudanar
da zanga zanga ne da nufin neman gwamnatin shugaban kasa Muhammadu Buhari ta
sako musu jagoransu, Ibrahim Zakzaky tare da matarsa. Majiyar Legit.ng ta
ruwaito dandazon yan shia’an sun yi shirin yin zaman dirshan a dandalin Eagle
Square ne, toh amma sai Yansandan kwantar da tarzoma suka ci musu birki, daga
bisani kuma suka gayyaci jagororin zanga zangar, Nura Marafa da Mujahid
Muhammad su fito su tattauna dasu.
Amma fitarsu keda wuya don tattaunawar sai Yansanda suka
shiga marinsu tare da jibgarsu, daga nan kuma suka yi awon gaba dasu, wannan ya
harzuka yan shia’an suka yi ca a kan Yansandan, inda su kuma suka harba musu
barkonon tsohuwa. Rahotanni sun bayyana da dama daga cikin yan shia’an sun
jikkata, wasu kuma sun suma a wajen.
Idan za’a tuna ko a ranar Laraba sai da aka kai gwauro aka
kai mari tsakanin Yansandan Najeriya da yan Shia a farfajiyar majalisar dokokin
Najeriya inda yan shia’an suka kai zanga zangarsu, tare da yin kokarin kutse
cikin majalisar. Sai dai Yansanda sun taresu, wanda hakan ya janyo tashin
hankali aka raunata wasu, wasu suka suma, tare da kona motoci da kuma lalata
wasu motoci da suka kai guda 50, daga cikin wadanda aka raunata akwai Yansanda
4 da yan shia da dama, yayin da yan shia’an suka ce an kashe musu mutane 2.
DAGA ISYAKU.COM
Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi