Legit Hausa
Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya amince da nadin Mista
Ahmed Bolaji Nagode a matsayin Darakta Janar na cibiyar horar da harkar wutar
lantarki na kasa (NAPTIN). A wata wasika da ke tabbatar da nadin daga
ma’aikatar wutar lantarki mai kwanan wata 18 ga watan Yuli, 2019 dauke da lamba
FMP/7858/I/126, nadin zai shafe tsawon shekaru hudu ne.
Sannan kuma ya fara aiki ne daga ranar 20 ga watan Yuni,
2019. An haifi Bolaji Nagode a ranar 10 ga watan Augusta, 1962, sannan ya yi
karatu a jami’ar Ahmadu Bello da ke Zaria, jami’ar Ilorin da kuma jami’ar
Lagas.
Bolaji ya kasance mataimakin Janar Manaja a kamfanin wutar
lantarki na Najeriya kafin daga bisani aka nada shi mataimakin darakta a
cibiyar NAPTINS a watan Fabrairun 2013. Ya kuma zama darakta a watan Fabrrairun
2014-2016. Ya kasance rike da mukamin mukaddashin darakta janar na NAPTIN tun
daga 2016 kafin wannan sabon nadin da aka yi masa.
DAGA ISYAKU.COM
Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi