Legit Hausa
Mukaddashin shugaban Alkalan Najeriya, Jastis Tanko
Muhammad, ya dira majalisar dokokin tarayyar domin amsa tambayoyi da tabbatar
da shi matsayin Alkalan alkalan Najeriya na din-din-din. Ya isa majalisar
misalan karfe goma da minti goma kuma a yanzu nan misalin karfe 11:09,
majalisar ta shirya shigowarsa cikin zauren majalisa.
Majalisar ta shiga ganawar sirri domin tattaunawa da Jastis
Tanko Mohammed da kuma tabbatar da shi. Wannan ya sabawa ka'ida da al'adar
majalisar saboda a zauren majalisa ake tantance duk wanda shugaban kasa ya
gabatar matsayin shugaban alkalan Najeriya.
A yanzu haka, Sanatocin sun dawo daga ganawar sirri kuma
mukaddashin Alkalin alkalan ya fara masa tambayoyi daga yan majalisan. A ranar
Alhamis, shugaba Muhammadu Buhari ya aika wasika majalisar dattawa inda ya
bukaci sanatocin sun tabbatar da Tanko Muhammad matsayin shugaban Alkalan
Najeriya na din-din-din.
Wannan ya biyo bayan takardar majalisar koli ta shari'a
wacce ta bukaci Buhari ya zamar da Tanko Mohammad cikakken Alkalin alkalai.
Shugaba Buhari ya nada Alkali Tanko Mohammed a watan Junairu bayan dakatad da
tsohon Alkalin alkalai, Walter Onnoghen, wanda aka tuhuma da zargin boye
kadarorinsa
DAGA ISYAKU.COM
Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi