Yanzu-yanzu: Kotun daukaka kara ta dakatar da shaidan Abba gida-gida


Legit Hausa

Kotun daukaka karar zaben gwamna dake zamanta a jihar Kano, ta dakatar da bukatar dan takarar gwamnan jihar na jam'iyyar PDP, Abba Kabiru Yusuf, ta gudanar da sauye-sauye a jerin sunayen shaidun da zasu tsaya masa a gabanta. Dan takarar gwamnan jihar Kano na jam'iyyar PDP, ya shigar da bukatarsa a gaban kotun na neman samun dama ta sauya kurarai a cikin jerin sunayen shaidun da za su tsaya masa a gabanta.

Abba K Yusuf na neman kotu da ta bashi damar kara sunayen wasu shaidu takwas kamar yadda jaridar The Nation ta ruwaito. Babban lauya mai wakilcin dan takarar na jam'iyyar PDP, Adegboyega Awomolo, ya ce babu wani nufi na sauya sunayen shaidun da suka gabatar face bukatar kara sunayen wasu shaidun takwas da a halin yanzu kotun ta ki amincewa.

Yayin shimfida dalilai da take zartar da hukunci, Mai shari'a Halima S. Muhammad, ta ce kotun ta yi watsi da wannan bukata ta jam'iyyar PDP duba da girma da kuma bijirowarta a kurarren lokaci da ya sabawa ka'ida ta shari'a. Har ila yau, dan takarar gwamnan jihar Kano na jam'iyyar PDP, Abba Kabir Yusuf, na ci gaba da kalubalantar nasarar da gwamna Abdullahi Umar Ganduje yayi a babban zaben kasa da ya gudana a watan Maris da ya gabata
 

DAGA ISYAKU.COM

Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN