Legit Hausa
A yanzu
haka majalisar wakilai ya kaure da hayaniya kan sanar da matsayin Shugaban
marasa rinjaye a majalisar. Rigiman ya fara ne kan hukuncin da kakakin
majalisar wakilai, Femi Gbajabiamila ya yanke shawarar yin jifa da wata wasika
daga jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) da ke zabar Kingsley Chinda a
matsayin Shugaban marasa rinjaye.
Kakakin
majalisar yayi gaban kansa wajen sanar da Ndudi Elumelu a matsayin Shugaban
marasa rinjaye, lamarin da ya haddasa zanga-zanga daga mambobin PDP. Wani dan
majalisa da ba a bayyana ba ya kwace sandar iko wanda hakan ya haddasa
hayaniya. Jam’iyyar adawa a wata wasika ta bayyana Mista Chinda a matsayin
shugabanta a majalisar wakilai.
Hukuncin
jam’iyyar na kunshe ne a wata wasika mai kwanan wata 26 ga Yuni sannan ta mika
ta zuwa ga kakakin majalisar. An tura wasika makamanciyar wannan zuwa majalisar
dattawa, kan wanda jam’iyyar ke so ya zama shugabanta inda ta zabi Eyinnaya
Abaribe a matsayin Shugaban masu rinjaye.
Jam’iyyar
ta kasance mara rinjaye a majalisar wakilan, sannan kuma daga Mista Chinda har
Elumelu mambobinta ne. Jam’iyyar PDP ta bukaci mambobinta da kada su zabi Mista
Gbajabiamila a lokacin da yake takarar kujerar kakakin majalisar. Sai dai ba a
san ko dalilin kakakin majalisar na aikata hakan na da nasaba da kokarin rama
abunda PDP tayi masa ba.
DAGA ISYAKU.COM
Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi