A kullun abubuwan ban-al’ajabi da mamaki na ci gaba da
faruwa a tsakanin mutanen wannan karni, har ta kai a yanzu zaman lafiya yayi
karanci a tsakanin ma’aurata harma da wadanda suka yi auran soyayya.
A baya-bayan nan an samu lamura da dama wanda ke nuna inda
mata ke sheka mazajensu lahira sakamakon sabani kowani rashin jituwa da ke
gibtawa a tsakaninsu. Hakan ne ya faru a tsakanin wasu ma’aurata a yankin
Darmnawa bayan gandun Sarki a birnin Kano, inda muka ji cewa wata uwargida ta
yi ajalin maigidanta sakamakon rashin jituwa da ya gibta a tsakaninsu.
Wani mai amfani da shafin Facebook, Ahmad Deedat ne ya
wallafa labarin, inda yace rikici ne ya fara kaurewa tsakanin matar da
makwabtansu akan fadan yayansu, ana cikin haka ne sai mijin ya dawo ya tarar
dasu.
Sai dai ba tare da bata lokaci ba mijin ya kora yaransa gida
tare da matar tasa, sa’annan ya baiwa makwabtan hakuri. haka ta shirya masa
mugunta. Sai dai hakan da maigidan yayi bai mata dadi ba saboda haka ta kulla
masa wani tuggu.
Yana shiga gida ta dauki wani katako ta rafka mashi ba
kakkautawa har ya yanke jiki ya fadi matacce.
DAGA ISYAKU.COM
Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi