Wani dan majalisan Dattawa ya shiga uku, Majalisa ta kafa masa kwamitin musamman


Legit Hausa


Shugaba majalisar dattawa, Ahmad Ibrahim Lawan, ya kafa kwamiti na musamman domin bincike cikin bidiyon da ya yadu a kafofin ra'ayi da sada zumunta wanda ke nuna sanata Elisha Ishaku, mai wakiltar Adamawa ta kudu yana dukan mace.

Wannan magana ya biyo bayan karar da da Sanata Uba Sani mai wakiltar Kaduna da tsakiya ta shigar a zauren majalisa da safiyar Laraba, 3 ga watan Yuli, 2019 inda ya bayyana yadda abin ke jawo cece-kuce a fadin kasa da duniya gaba daya. Sanata Uba Sani ya bukaci majalisar dattawan tarayya da dau matakin hukunta Sanata Elisha Abbo, kan wannan abin kunyan da yayi wanda ka iya batawa majalisar suna.

Shugaban majalisar dattawa a jawabinsa ya bayyana cewa wannan zargi ne tukunna amma sai an gudanar da bincike kafin a tuhumesa. Yace: "Da safen nan na samu kiraye-kiraye da dama daga cikin gida Najeriya da kasashen wajen kan abinda ya faru.

Bisa ga wadannan kiraye-kiraye da bacin ran da yan Najeriya suka nuna da kuma jawaban abokan aikinsa, na nada kwamitin domin binciken zargin zaluncin da ake yiwa Sanata Elisha Abbo."
 

DAGA ISYAKU.COM

Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews

 Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN