A wata hira da jaridar Aminiya ta yi da fitacciyar jarumar
wasan Hausa ta Kannywood, Fatima Isah Muhammad wacce aka fi sani da Teema Yola.
Ta bayyana yadda ta yi suna a duniyar fim Jarumar wacce ta fito da sunan Hajiya
Laure a cikin fitaccen fim dinnan na Mansoor, wanda ya zama daya daga cikin
manyan fina-finai da aka taba yi a masana'antar Kannywood. Yanzu haka dai
tauraruwar jarumar na kara haskawa a duniyar fim.
Ga yadda hirar ta su ta kasance da jaridar Aminiya:
Aminiya: Ya aka yi kika fara wannan sana'a?
Teema: Na shiga harkar fim ne saboda ina sha'awar sana'ar
sosai. Ban taba boye soyayyar da nake yiwa kaina na ganin na zama jaruma ba,
kuma sai nayi sa'a daya daga cikin manyan marubutan masana'antar, Abdulkarim
Papalaje sai ya hada ni da wasu masu shirya fina-finai na masana'antar. Suka
gwada ni, da yake abu ne da nake so sosai sai gashi na basu mamaki sosai. Yanzu
maganar nan da nake daku ban san iya fina-finai nawa na fito a cikinsu ba. Na
san shaharar da nayi a masana'antar ba yin kai na bane, yin Allah ne, kuma ko
da yaushe ina yi masa godiya da wannan ni'ima da yayi mini; wannan ita ce
shekarata ta bakwai a wannan masana'anta.
Aminiya: Gaya mana irin fadi tashin da kika sha a wannan
masana'anta?
Teema: Na sha fama sosai kafin na samu damar shigowa wannan
masana'anta. Akwai lokuta da dama da za a sanya ni a fim, bayan anyi an gama
komai, a karshe sai a hanani kudina. Zan iya yina akan a biya ni, amma wallahi
baza su biya ni ba. A lokuta da dama, mutane sukan bani shawarar na shigar da
kara, amma kawai sai nayi dariya na manta da zancen. Daga baya sai na zo na
gane cewa ana yi mini haka ne saboda ni sabuwar 'yar wasa ce, amma yanzu mutanen
da suke hanani kudin nawa a da sune suke fara biyana tun kafin ma a fara shirin
fim din.
Aminiya: Wasu na cewa ana biyan ki da tsada kafin ki yadda
ki fito a fim, shin gaskiya ne?
Teema: Dan kana tuka mota mai tsada, ko kana siyan abubuwa
masu tsada ba hakan ne yake nuna cewa kai kai mai tsada bane a wajen aikin ka.
Ni jaruma ce da nake kokarin ganin na kare mutuncina a koda yaushe, ina jin
hakan ne yasa mutane suke mun wani kallo na daban.
Aminiya: Me zaki ce game da cigaban da kika samu a
matsayinki na jaruma?
Teema: Cigaban dana samu a masana'antar Kannywood suna da
yawa, amma zan iya cewa na je wurare masu yawan gaske, wadanda inda ace ban
shiga harkar fim ba babu yadda za ayi naje wadannan wurare. Na hadu da manyan
mutane da kuma masoya wadanda suke son ganin sun yi mini duk abinda nace ina
so.
Aminiya: Hakan na nufin kin gama cimma burinki na rayuwa
kenan?
Teema: Eh kusan haka, amma babban burina shine naga nayi
aure na zauna a gidan mijina. Amma kuma ba zan daina harkar fim ba koda nayi
aure. Zan cigaba da zama tare da masana'antar amma ba a matsayin jaruma ba. Zan
zama mai bada umarni. Amma kuma hakan ya danganta da yadda mijina yake so ya
ganni; idan yace yana so na zauna a gida babu damuwa zan zauna. Aminiya: Wani
abu ne na bakin ciki da ya taba faruwa dake a wannan masana'anta?
Teema: Wani abu ya taba faruwa dani a lokacin ina sabuwar
jaruma. Nayi kwanaki bakwai ana daukar mu a wani shirin fim, a lokacin har
kunama sai da ta cije ni, amma a karshe aka ki biyana hakkina. Na sha wahala
matuka a lokacin daukar wannan fim. Ina jin ba dadi a duk lokacin dana tuna da
wannan lokaci.
Aminiya: Kina da wani sako ne ga da zaki bayyana ga
masoyanki?
Teema: Ina so masoyana su san cewa babu wani abu da yake
zama har abada, saboda haka ina so suyi amfani da damarsu a lokacin da suke da
ita kafin ta wuce. Kuma ina so su cigaba da nuna mana soyayya, mu kuma munyi
alkawarin ba za mu bari su ji kunya ba.
DAGA ISYAKU.COM
Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi