Ta faru! Amaechi ya fede biri har wutsiya, ya bayyana 'yan siyasar da suka sace kudi suka azurta kansu a kasa


Legit Hausaa

Tsohon ministan sufuri, Rotimi Amaechi, ya bayyana cewa Najeriya kasa ce da ba a damu da bin doka ba, inda ya kara da cewa 'yan Najeriya basa ganin laifin 'yan siyasa akan matsalar talaucin da suke ciki. Amaechi ya bayyana cewa ya san 'yan siyasar da kafin su samu mulki basu da ko anini, amma suna hawa mulki suka mayar da kansu hamshakan masu kudi.

Da yake magana a wajen wani taro da aka yi akan matasan 'yan siyasa masu tasowa a jihar Legas, Amaechi ya ce akwai bukatar 'yan siyasa su bayyana yadda suke so fitar da mutane daga cikin kangin talaucin da suke ciki. a ce: "Na san 'yan siyasar da suka saci makudan kudade suka azurta kansu, kuma wannan kudade da suka sata kamata yayi ayi amfani da su wajen gina hanyoyi da sauran ayyukan more rayuwa ga al'umma.

"Ya kamata 'yan siyasar mu su fito karara su bayyanawa al'umma hanyoyin da zasu bi su fitar dasu daga cikin wannan kangin talaucin da suke ciki."
 

DAGA ISYAKU.COM

Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN