Legit Hausaa
Tsohon ministan sufuri, Rotimi Amaechi, ya bayyana cewa
Najeriya kasa ce da ba a damu da bin doka ba, inda ya kara da cewa 'yan
Najeriya basa ganin laifin 'yan siyasa akan matsalar talaucin da suke ciki.
Amaechi ya bayyana cewa ya san 'yan siyasar da kafin su samu mulki basu da ko
anini, amma suna hawa mulki suka mayar da kansu hamshakan masu kudi.
Da yake magana a wajen wani taro da aka yi akan matasan 'yan
siyasa masu tasowa a jihar Legas, Amaechi ya ce akwai bukatar 'yan siyasa su
bayyana yadda suke so fitar da mutane daga cikin kangin talaucin da suke ciki.
a ce: "Na san 'yan siyasar da suka saci makudan kudade suka azurta kansu,
kuma wannan kudade da suka sata kamata yayi ayi amfani da su wajen gina hanyoyi
da sauran ayyukan more rayuwa ga al'umma.
"Ya kamata 'yan siyasar mu su fito karara su bayyanawa
al'umma hanyoyin da zasu bi su fitar dasu daga cikin wannan kangin talaucin da
suke ciki."
DAGA ISYAKU.COM
Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi