Legit Hausa
Wani matashi, Nsisong Okon Etim, mai shekaru 27, ya kashe
kansa a garin Efiat Ikot Edo a karamar hukumar Uyo da ke jihar Akwa Ibom bayan
ya yi zargin cewa mahaifiyarsa da dan uwansa da mutumin da yake haya a gidansa
na yawan damunsa.
Marigayin, wanda ya kammala karatunsa na jami'a' ya bayyana
hakan ne a cikin wata takarda da ya rubuta kafin mutuwarsa. "Na katse
rayuwata ne saboda bakin ciki, domin na samar wa kai na sauki daga damu da
damuwar da mahaifyata, dan uwana da mutumin da nake hayar sana'ar siyar da
makamashin 'gas' a shagonsa ke saka ni koda yaushe, kamar yadda Nsisong ya
rubuta.
Batun mutuwar matashin na cigaba da girgiza mazauna titin
Ukpong Edet inda marigayin da mahaifiyarsa ke zaune. Wata majiya daga dangin
marigayin ta bayyana cewa matashin ya kammala hidimar kasa tun shekarar da ta
gabata kuma ya fara sana'ar sayar da makamashin iskar 'gas' bayan ya gaza samun
aikin gwamnati.
Yar uwar marigayi Nsisong ta bayyana cewa marigayin ya
kasance mai zurfin ciki da ba ya son tattauna matsalolinsa da kowa. Nsison ya
kashe kansa ne ranar Talata, 23 ga watan Yuli, ta hanyar rataye kansa a jikin
wata igiya da ya daura a rufin dakinsa bayan ya tube daga shi sai dan kamfai.
Sai dai mahaifiyarsa, wacce ke cikin matukar halin dimuwa, ta kasa cewa komai
ga manema labarai yayin da take ta zubar da hawaye a lokacin da aka binne
Nsisong.
DAGA ISYAKU.COM
Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi