Legit Hausa
An dage sauraron karar da ‘dan takarar shugaban kasar
Najeriya na zaben 2019 a jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya kai gaban kotun koli
inda ya ke kalubalantar shari’a da a ke yi a kotun zabe. A Ranar 30 ga Watan
Yuli, 2019, babban kotun Najeriya ta dage zaman da ta ke yi domin sauraron
korafin da Atiku Abubakar ya kawo na neman a yi watsi da hukuncin da Alkali
Garba Muhammad ya yi.
Babban Lauyan ‘dan takarar na PDP, Paul Erokoro, ya nemi
kotu ta karbi wasu karin hujjoji da bayani daga gare sa. Wannan ya jawo
shari’ar ta tsaya cak inda sauran Lauyoyi su ka nemi a kara masu lokaci. A wani
mataki da kotun ta fara dauka, za a dakatar da zaman wannan shari’a sai zuwa
Ranar 20 ga Watan gobe na Agusta. Alkali mai shari’a Mary Peter-Odili da wasu
Alkalai su dauki wannan hukunci.
A Ranar jiya Talata ne mai shari’a Mary Peter-Odili ta nemi
a dakatar da sauraron wannan kara zuwa nan da mako uku. Kafin wannan lokaci
wadanda a ke tuhuma za su kammala duk binciken da su ke yi. Babban Alkalin da
ke sauraron korafin zaben shugaban kasa na 2019, Mai shari’a Garba Mohammed ya
yi watsi da wani roko da Lauyoyin PDP su ke yi na bada dama su duba uwar-garken
INEC.
Jam’iyyar PDP ta hakikance a kan cewa ita ce ta lashe zaben shugaban
kasa kamar yadda kuri’un da hukumar zabe na INEC ta tattara a uwar-garken ta su
ka nuna. INEC ta karyata wannan ikirari a gaban kotu. Yunus Usman shi ne Lauyan
da ke kare hukumar zabe a kotu, yayin da shi kuma babban Lauya Wole Olanipekun,
ya ke kare shugaban kasa. Lateef Fagbemi, shi ne Lauyan APC a wannan kara.
DAGA ISYAKU.COM
Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi