Legit Hausa
Wata mata mai suna Bilkisu Isah ta jibgi mijinta, uban
yayanta da wani makeken icce a gidansu dake unguwar Sabon Tahsa cikin garin
Abaji na babban birnin tarayya Abuja, inda nan take ya fadi matacce. Jaridar
Daily Trust ta ruwaito wani makwabcin ma’auratan mai suna Salihu ya bayyana
cewa lamarin ya faru ne a ranar Alhamis data gabata da misalin karfe 9:12 na
dare sakamakon sa-in-sa data kaure tsakanin ma’auratan.
A cewar Salihu, Mijin matar mai suna Isah Egba ya rufe
Bilkisu da fada ne akan fita da tayi daga gidansu ta bar yayansu 5 suna
gararamba, kuma ba tare da neman izininsa ba, har sai karfe 8 na dare ta dawo,
daga nan sai ya umarceta daga fitan masa daga gida.
Malam Isah bai tsaya nan ba sai ya rarumi uwargida Bilkisu
da nufin fitar da ita da kansa daga gidan, hakan ne ya bata ma Bilkisu rai,
inda ta rarumi wani katon icce ta maka masa a kai, nan take ya yanke jiki ya
fadi, jini na ta kwarara daga kansa. Makwabtansu ne suka yi kokarin garzayawa
dashi zuwa Asibitin Abaji cikin gaggawa, inda daga nan aka mikashi zuwa
asibitin koyarwa na jami’ar Abuja, amma bai yi tsawon rai ba, inda ya cika a
cikin daren.
Da majiyar Legit.ng ta tuntubi rundunar Yansandan Abuja don
jin ta bakinsu, sai kaakakinta, DSP Anjuguri Manzah ya tabbatar mata da aukuwar
lamarin, kuma yace sun kaddamar da bincike akan lamarin, amma a yanzu suna
farautar uwargida Bilkisu bayan ta ranta ana kare.
DAGA ISYAKU.COM
Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi