Legit Hausa
Tsohon gwamnan jihar Zamfara, Abdulaziz Yari ya cacaki
tsohon shugaban Najeriya Olusegun Obasanjo kan budaditar wasikar da ya rubuta
ga Shugaban Kasa Muhammadu Buhari. Mista Obasanjo ya fitar da wasikar ne a
ranar Litinin inda ya ke yi wa Buhari gargadi kan halin tarbarbarewar tsaro da
rarrabuwar kan al'umma a kasar.
Obasanjo ya zargi shugaban kasar da nuna halin in kula kan
da rashin daukan mataki kan kallubalen da suke tasowa a kasar. A sanarwar da ya
fitar da hannun hadiminsa na kafafen yadda labarai, Ibrahim Dosara, Yari cacaki
Mista Obasanjo da wasu shugabanin Yarabawa ta bai bayyana sunayensu ba kan
sukar yadda Buhari ke tafiyar da harkar tsaro a kasar.
Tsohon gwamnan ya yi zargi tsohon shugaban kasar da yin
amfani da wannan damar ne don huce fushin da ya ke fama da shi kan Buhari inda
ya ce tsohon shugaban kasar bai aikata wani abin azo a gani da ta fi na Buhari
ba a zamaninsa.
"Kowa ya san
cewa a zamanin Shugaba Olusegun Obasanjo ne aka yi wa mutane Zaki Biam na jihar
Benue da Odi a Bayelsa kisar kiyashi. "Babban rikicin 'Yan Shi'a na Kaduna
ma ta faru ne a karkashin mulkinsa. Kuma lokacin mulkinsa ne aka shuka rikin
Plateau.
Kamar ya manta dukkan wadannan abubuwan da suka faru a
zamaninsa. Ya kuma manta da kisar gillar da aka yi wa tsohon minista Bola Ige
da jigo na jam'iyyar adawa Harry Marshall," inji shi. Ya ce babu laifi a
nuna bacin rai kan kisar da aka yi wa Mrs Funke Olakunrin, diyar shugaban
kungiyar Afenifere, Reuben Fasoranti, ya yi tir da yadda wasu ke sauya maganar
suke cewa makiyaya Fulani ne suka aikata kisar.
DAGA ISYAKU.COM
Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi