Legit Hausa
Shahararren malamin addinin Musuluncin nan da yayi kaurin
suna wajen sukan gwamnatin shugaban kasa Muhammadu Buhari, Ahmad Gumi ya fara
bin manya a Najeriya domin su sanya baki tare da kira ga shugaban kasa ya saki
shugaban yan shia, Ibrahim Zakzaky.
Gumi ya yi wannan yunkuri ne duba da tarzomar da cigaba da
rike shugaban yan shia, Ibrahim Zakzaky ke janyowa a babban birnin tarayya
Abuja, da kuma gudun abinda ka iya faruwa a Najeriya gaba daya idan har
gwamnati ta cigaba da rikeshi. Jaridar Desert Herald ta ruwaito a kokarin ganin
an shawo kan matsalar ne Sheikh Ahmad Gumi ya yi takanas ta Kano zuwa gidan
jagoran APC, Sanata Ahmad Bola Tinubu, inda ya samu ganawa dashi, tare da yi
masa magiya a kan ya yi ma Buhari magana don ya sako El-Zakzaky.
A yayin zaman tattaunawa, Gumi ya nanata ma Tinubu
matsalolin da ka iya faruwa idan har gwamnatin Buhari ta cigaba da rike Zakzaky
duk da rashin lafiyar da yake fama dashi, ga shi kuma wasu kotuna sun bada
umarnin a sakeshi. Majiyarmu ta ruwaito bayan sauraron jawabin malamin, sai
Tinubu ya bashi tabbaci tare da alkawarin zai isar da sakonsa ga shugaban kasa
Muhammadu Buhari.
Baya ga Gumi, shima babban malamin darikar Tijjaniyyah,
Sheikh Dahiru Usman Bauchi, ya yi irin wannan kira a baya ga Buhari. Wannan
zama mai muhimmanci da Gumi ya yi da Tinubu ya tabbata ne ta hannun tsohon
shugaban EFCC, Nuhu Ribadu, wanda shi ne ya hada wannan ganawar sirri tsakanin
shuwagabannin biyu.
DAGA ISYAKU.COM
Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi