Legit Hausa
Gwamnatin Jihar Sokoto ta ce tana tattaunawa da 'yan bindiga
da sauran wadanda suke kai hare-hare da iyakar jihar ta. Direkta Janar na Yadda
Labarai da Hulda da Jama'a na Gwamna Aminu Waziri Tambuwal, Abubakar Shekara ne
ya bayyana wa Daily Trust hakan jiya Alhamisa a garin Sokoto. A cewar Shekara,
an fara ganin amfanin tattaunawar da ke yi inda 'yan bindigan suka fara sako
wasu mutane da su kayi garkuwa da su a ranar Talata.
"Muna sa ran za a samu nasarar idan aka cigaba da
sulhun duba da cewa 'yan bindiga da dama da shugabanin su sun amince za su
ajiye makamansu," inji shi. Ya yi kira ga mutanen da su ke barin
kauyukansu saboda tsoron hari a sassan jihar su zauna a gidajensu saboda 'yan
bindigan sun tabbatarwa gwamnati cewa za su dakatar da kai hare-hare.
Shekara ya kuma yi kira ga al'ummar jihar su guji cin
mutuncin 'yan uwansu makiyaya Fulani a garuruwa da kasuwanin kauye. "Ya
zama dole mu cigaba da zaman lafiya kamar yadda aka san mu da shi," inji
shi. Majiyar Legit.ng ta ruwaito cewa al'ummar kauyukkan Isa da Sabon Birni a
karamar hukumar Goronyo duk sun tsere saboda yawan hare-haren da 'yan bindigan
ke kai musu. Rahotanni sun bayyana cewa a kalla mutane 60 ne 'yan bindiga suka
kashe a jihar Sokoto a wannan shekarar. An kashe 26 a watan Janairu a garin Gandi
da ke karamar hukumar Rabah.
A watan Fabrairu kuma an kashe wasu mutane 16 a Dalijan,
Rakkoni da Kalhu duk dai a karamar hukumar Rabah. Daga baya-bayan nan kuma an
kashe mutane 20 a Kamitau Mala Faru da Dan Tatsoko a karamar hukumar Goronyo.
DAGA ISYAKU.COM
Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi