Daga Abuja amaryata ta gayyato wani kato suka kama daki a Otal - Mutumin da uwargidarsa ta caka mai wuka ya yi tonon silili

Daga Abuja amaryata ta gayyato wani kato suka kama daki a Otal - Mutumin da uwargidarsa ta caka mai wuka ya yi tonon silili Read more: https://hausa.legit.ng/1248128-daga-abuja-amaryata-ta-gayyato-wani-kato-suka-kama-daki-a-otal---mutumin-da-uwargidarsa-ta-caka-mai-wuka-ya-yi-tonon-silili.html

Legit Hausa

Mutumin da uwargidarsa ta kusa hallakashi da wuka, Said Hussein, ya fito duniya yana fallasa amaryarsa kan irin iya shegen da take shekawa da ya kaiga dukanta har tayi nufin hallakashi. Sa'id Hussein bayan samun lafiyarsa ya bayyana cewa sau talatin yana kama matarsa tana turawa wasu mazaje ajnabiyya hotunan tsiraicinta a kafofin ra'ayi da sada zumunta. Idan ba a manta ba dai, Fatima Hanan ta cakawa maigidanta wuka ne a ranar 22 ga Yunin wannan shekara cikin tsakar dare da misalin karfe 1:30, a Unguwar Mai Kalwa, Na’ibawa, karamar Hukumar Kumbotso, a Jihar Kano.

 Kazalika, a cewarsa: " Ina da cikakkiyar shaida ta yadda Matata ta gayyaci wani saurayi nata daga Abuja, ya zo suka tare da ita a wani Otel da ke Unguwar Bompai, wanda dai kawai ba na son kama suna." "Amma dai wannan abu ya faru ne, a 26 ga watan Afrilun 2016, ba tare da la’akarin cewa ita matar aure ba ce.

Tana cikin wannan Otel daga misalin karfe 10:13 na safe har zuwa 12: 16 na rana, ina nan da wadannan bayanai, don kuwa na’urar CCTV ta wannan Otel ta nadi kafatanin wadanan bayanai da na ke fada a hali yanzu”, a cewar tasa. Hussain ya ci gaba da cewa, a ranar wannan Juma’a dai da wannan abu ya faru, na kama Hanan tana shan wasu kwayoyi a gidana tare da Shisha ta hada shi da wani sinadarin kayan maye.

 Sannan a ranar Azimin karshe, ta zuba min guba a abincina, ta hanyar kada wa a cikin kwai kafin ta soya, wannan ma ina da cikkakiyar shaida a kai." "A lokacin da abubuwa suka yi tsamari ne, muka nemi Dakta Bashir, Limamin Masallacin Alfurkan, ya shiga tsakani ya kuma ba mu shawarwari don gyaruwar al’amuran."

“A lokacin da muka je ganin Dakta Bashir tare da Matar tawa, Mahaifiyar da yayanta dukkanin su a cikin motata na dauke su muka tafi tare. "A gabansu ne kuma na zayyana wa Dakta Bashir irin miyagun halayenta musamman a bangaren rashin kula da addini da kuma shaye-shaye ta kuma amsa ko kadan ba ta musa ba." Amma Hanan, a wannan rana bayan mu dawo gida ne kuma ta aika min wannan aika-aika da wuka bayan na kwace wayarta wadda take tura wa samari da hotuna da kuma bidiyonta na batsa."
 

DAGA ISYAKU.COM

Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN