Da zafi-zafi: Yan Shi’a sun gudanar da zanga-zanga a Masallacin Abuja


Legit Hausa

Mambobin kungiyar Musulmai yan Shi’a sun gudanar da zanga-zanga a wani masallaci a Zone 3, Abuja, inda suka nemi saki shugabansu Sheikh Ibrahim El-Zakzaky da matarsa. Kungiya tau ma bayyana cewa wasu daga cikin mambobinsu da rundunar yan sanda Najeriya ta kama sun mutu aa tsare a rundunar tsaron.

Daya daga cikin shugabannin kungiyar, Abullahi Musa, wanda ya zanta da manema labarai, ya bayyana da faro cewa za a fara zanga-zangar ne da zaran an kammala sallar Juma’a.

Kan mutuwar mambobinsu,Musa yace: bayanai abun dogaro da ke zuwa mana ya bayyana cewa yan sandan Najeriya sun tsare mambobin da ke zanga-zangar a saki Zakzaky ciki harda mata da kananan yara, tun ranar Ltinin, 2 a watan Yuli, tare da raunuka da ke barazana ga rayuwarsu sannan sukahana masu abinci da ganin likita.

“Zuwa yanzu,mutum uku sun mutu a hanun yan sanda saboda rashin kulawar ikita. Kamata yayi ace an kai masu zanga-zagar kotu cikin kasa da sa’oí 24,amma sun kwashe mako guda cur a hannun yan sanda." Idan za kutuna a ranar Litinin, 22 ga watan Yuli ne rikici ya kaure tsakanin yan sanda da Shi’a a lokacin wata zanga-zanga a sakatariya tarayya, Abuja wanda yayi sanadiyar mutuwar mutane da dama.
 

DAGA ISYAKU.COM

Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN