Legit Hausa
Yan bindiga sun harbe kawun sanata Elisha Abbo, sanatan da
aka gani a wani bidiyo ya na dukan wata mata a shagon siyar da kayan jima’i na
robobi. Yan bindigan sun kuma yi awon gaba da goggon sanata Abbo da ke shayarwa
a harin da suka kai yau Asabar 13 ga watan Yuli 2019 a jihar Adamawa.
Hukumar yan sanda da jama’ar garin sun bayyana cewa an kai
harin a Muchalla dake a karamar hukumar Mubi ta arewa dake a jihar Adamawa. Yan
uwa da abokan arzikin goggon sanata Abbo sun bayyana cewa ta haihu kimanin
kwanaki 11 da suka wuce.
Mutanen garin sun bayyana ma jaridar Premiumtimes ta wayar
salula da misalin karfe 1:00 na rana, inda wani mutum da abin ya faru akan
idonshi ya bayyana cewa bayan da yan bindigan suka shigo gari sai suka “Tunkari
gidan iyalan sanata Abbo kai tsaye inda suka dauke goggonshi dake shayarwa. Ta
haihu kimanin kwana 11 da suka wuce.”
“A lokacin da suke kokarin tserewa, kawun Abbo ya fito daga
cikin dakinshi, bayan da ya gansu sai yayi kokarin sanar da jama’a. Nan take
yan bindigan suka bude mashi wuta wanda hakan yayi sanadiyyar mutuwarshi su
kuma suka tsere.
A yanzu haka ana ta jimami a kauyen.” Mai magana da yawun
rundunar yan sanda na jihar Adamawa, Sulaiman Nguroje, ya tabbatar da afkuwar
lamarin. Ya bayyana cewa an tura yan sanda su bi sawun yan ta’addan.
Ya bayyana cewa “An tura yan sanda na musamman na babban
sifeton yan sanda tare da yan sanda masu yaki da garkuwa da mutane da bangaren
kisa don su ceto wadda aka yi garkuwa da ita su kuma kama yan ta’addan.”
DAGA ISYAKU.COM
Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi