Legit Hausa
Gungun yan bindiga sun yi awon gaba da wwargidar shugaban
hukumar karamar hukumar Paikoro na riko, Alhaji Sani Balarabe, Malama Suwaiba
Balarabe da nufin yin garkuwa da ita har sai an biya kudin fansa kafin su
saketa.
Jaridar Daily Trust ta ruwaito mijinta, Alhaji Sani, yaya ne
ga shugaban ma’aikatan fadar gwamnatin jahar Neja, Alhaji Ibrahim Balarabe,
rahoton ya kara da cewa an yi garkuwa da Suwaiba ne a ranar Talata, 16 ga watan
Yuli. Majiyar Legit.ng ta ruwaito yan bindigan sun yi awon gaba da Suwaiba ne
tare da wata kawarta, matar manajan wani kamfani mai zaman kansa dake garin
Kagara, cikin karamar hukumar Rafi na jahar Neja.
TALLATA HAJARKA A ISYAKU.COM domin isar da kasuwancinka ga mutum miliyan 3.5 a Najeriya da nahiyar Afrika. Tuntube mu a yau a isyakulabari@gmail.com
Majiyar ta ruwaito cewa yan bindigan sun kai farmaki cikin
garin ne suna ta harbe harbe, inda kai tsaye suka zarce gidan manajan kamfanin,
suka yi kokarin tafiya da dansa, amma matarsa ta rokesu su kyale danta su
dauketa.
Daga nan kuma sai suka haura katangar gidan shugaban
hukumar, jin hakan yasa matar shugaban hukumar ta garkame kanta a cikin bayan
gida, amma a dole ta fito bayan yan bindigan sun yi barazanar kashe yan uwanta
dake gidan.
Wani majiyar na karkashin kasa ya bayyana cewa yan bindigan
sun shaida ma matar cewa mijinta suke nema, amma tunda basu sameshi ba zasu
tafi da ita, sa’annan sun nemi a biyasu naira miliyan 100 kafin su saketa.
Kaakakin rundunar Yansandan jahar, DSP Muhammad Dan-Ina Abubakar ya tabbatar da
aukuwar lamarin, kuma yace suna iya kokarinsu don ceto mutanen da yan bindigan
suka yi awon gaba dasu.
DAGA ISYAKU.COM
Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi