Buhari ya bukaci majalisar ta amince da nadin Farfesa Galadima a matsayin shugaban NIPSS

Legit Hausa
Shugaban kasa, Muhammadu Buhari, ya bukaci majalisar dattijai ta amince da nadin Farfesa Habu Galadima a matsayin sabon babban darektan cibiyar horon manyan jami'an gwamnati (NIPSS) da ke Kuru, a Jos, jihar Filato.
Shugaban majalisar dattijai, Dakta Ahmad Lawan, ne ya karanta wasikar da shugaban kasar ya aiko zuwa majalisar yayin zaman ta na ranar Talata.
Buhari ya ce sashe na 8 (5) na dokokin NIPSS ne ya bashi ikon rubuta wasikar da ya aika wa majalisar a ranar 9 ga watan Yuli.
Ya bukaci mambobin majalisar su bashi hadin kai wajen tabbatar da nadin Farfesa Galadima a matsayin shugaban NIPSS ba tare da wata matsala ba.
Shugaban kasar ya hada da takardun Farfesa Galadima da ke dauke da irin karatun da ya yi da kuma gogewarsa a aiki da kuma dukkan wasu bayanai da zasu taimaka wa majalisar wajen tantance shi.
Kamfanin dillancin labarai na kasa (NAN) ya rawaito cewa an haifi Galadima a shekarar 1963 a karamar hukumar Toto da ke jihar Nasarawa.
Yanzu haka Galadima farfesa ne a fannin kimiyyar siyasa a jami'ar Jos, jihar Filato, inda ya yi digirinsa na farko; a shekarar 1987, da na biyu(MSc); a shekarar 1990, da na uku (PhD); a shekarar 2006.
Farfesa Galadima ya rike shugaban sashen karatun kimiyyar siyasa a jami'ar Jos, sannan ya taba aiki da kungiyar kasashen Afrika ta yamma (ECOWAS) da bankin duniya da wata kungiyar majalisar dinkin duniya (UNDP)
DAGA ISYAKU.COM Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN