Legit Hausa
Wani jami’in hukumar tsaro ta farin kaya, Civil Defence ya
hana babban alkaliyar jahar Kebbi, kuma shugaban Alkalan jahar dake rike da
rikon mukamin Alkalin Alkalan jahar, Elizabeth Karatu daga shiga kotu a ranar
Alhamis din data gabata.
Hakan ya bayyana ne cikin wani bidiyo dake yawo a kafafen
sadarwar zamani, inda aka hangi jami’in da kuma dogarin Elizabeth, wanda shima
jami’in Dansanda ne suna cacar baki akan hana Elizabeth shiga kotu don ta yanke
hukunci.
Duk kokarin da Dansandan dogarin Alkaliyar ya yi na ganin ta
samu shiga kotun domin ta yanke hukunci na karshe a wani shari’a dake gabanta,
ya ci tura, sakamakon jami’in yace umarni aka bashi kada ya barta ta shiga
kotu.
Dama dai akwai jikakkiya tsakanin Elizabeth da gwamnatin jahar, inda ta yi zargin gwamnan jahar ya ki tabbatar da ita a matsayin Alkalin Alkalan jahar Kebbi saboda it aba Musulma bace, duk da cewa majalisar dokokin jahar ta tabbatar da cancancarta.
Rashin tabbatar da ita wannan mukami ne ya kawo rikici
tsakanin gwamnati da ita, wanda har ta kai ga ta kai karar gwamnan jahar ga
majalisar sharia ta koli, amma duk da sanya baki da majalisar ta yi Gwamna
Bagudu bai tabbatar da ita ba.
Da yake tsokaci game da bidiyon, shugaban kungiyar lauyoyi
reshen jahar Kebbi, Husseini Zakariya ya bayyana cewa ya kalli bidiyon, kuma
zasu kafa kwamitin bincike domin gudanar da cikakken bincike game da lamarin
tare da gano musabbabin aukuwar lamarin. Sai dai shugaban hukumar NSCDC,
Abdullahi Muhammad Gana ya bayyana cewa jami’insu bai yi wani laifi daya hana Elizabeth
shiga kotu ba, domin a cewarsa kotun a garkame yake a lokacin, don haka aikinsa
yake yi a wannan lokaci.
DAGA ISYAKU.COM
Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi