Legit Hausa
Rundunar soji ta kori wasu jami'anta 8 daga aiki bayan an
zarge su da guduwa daga sansanin su bayan mummunan harin da mayakan kungiyar
Boko aram suka kai kan rundunar soji ta 157 a kauyen Metele da ke karamar
hukumar Guzamala a jihar Borno.
Sojoji da dama da suka hada kwamanda, Laftanal Kanal Ibrahim
Sakaba, sun rasa ransu sakamakon harin da aka kai sansanin sojin a watan
Nuwamba na shekarar 2018. Jaridar Sunday Punch ta rawaito cewa an gano sojoji
sun gudu ne bayan an gudanar da kidaya a sansaninsu.
Wasu daga cikinsu sun bayyana bayan wata guda da kai harin.
A ranar 19 ga watan Afrilu, mukaddashin kwamandan rundunar soji ta 157, Manjo
UI Lezuya, ya bayar da umarnin gudanar da bincike domin gano dalilin bacewar
sojoji da kuma bayyanarsu daga baya.
Wata majiya daga cikin rundunar soji ta ce binciken da aka
gudanar ya hada gano lokacin da sojojin suka bar sansanin, dalilinsu na yin
hakan da kuma dalilin dawowarsu bayan shafe kwanaki basa nan da me suke yi
bayan a tsawon lokacin da basa sansanin.
Ragoar abinda bincike ya shafa sun hada da gano inda sojojin
suka ajiye bindoginsu ko kuma sun dawo tare da su bayan shafe lokaci mai tsawo
basa sansaninsu da kuma sanin ko rundunar da suke ciki tayi wani kokari wajen
bayar da shawarar a hukunta su bayan sun gano cewar basa nan.
Wata babbar majiya daga cikin mahukunta a rundunar soji ta
bayyana cewa kwamitin mutum biyar da aka kafa ya samu sojojin da aikata laifin
da ake tuhumarsu da aikata wa, wanda a saboda haka kuma aka kore su daga aiki.
Duk da majiyar ba ta ambaci sunayen sojojin ba, ta bayyana cewa hukuncin ya yi
tsauri.
DAGA ISYAKU.COM
Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi