Legit Hausa
A yayin ci gaba da kalubalantar sakamakon babban zaben kasa
na 2019, dan takarar kujerar shugaban kasa na jam'iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya
gano wani bakin tuggu da fadar shugaban kasa ke kullawa domin cin galaba a
kansa a gaban kotun daukaka kara.
Atiku da kungiyar sa ta kwararrun lauyoyi na ci gaba da
zargin fadar shugaban kasa da kawo jinkirin fara sauraron karar sa ta
kalubalantar sakamakon zaben kasa domin cimma manufa ta watsi da karar sa. Dan
takarar kujerar shugaban kasa na jam'iyyar PDP, ya shigar da koken sa a gaban
shugabar kotun daukaka kara, Jastis Zainab Bulkachuwa, kan kawo jinkiri gabanin
fara sauraron karar sa ta kalubalantar sakamakon zaben shugaban kasa da aka
gudanar a ranar 23 ga watan Fabrairu.
Tsohon mataimakin shugaban kasa ya shigar da korafin sa
cikin wata rubutacciyar wasika ta ranar 31 ga watan Mayun 2019 da sanadin daya
daga cikin lauyoyin sa, Silas Joseph Onu, da ya ce hakan na zuwa ne da umurnin
jagoran kungiyar su ta lauyoyi, Levi Uzokwu. Ko shakka babu an samu jinkirin ci
gaba da shirye-shiryen fara sauraron karar Atiku ta kalubalantar sakamakon
zaben shugaban kasa yayin da babbar Alkaliya mai shari'a, Zainab Bulkachuwa ta
zame hannu ta daga shari'ar.
Legit.ng ta fahimci cewa, domin tsarkake kanta daga tantamar
nuna wariya ko kuma rashin gaskiya, Jastis Bulkachuwa ta zame hannun ta kwanaki
11 da suka gabata biyo bayan nasarar mai gidanta ta lashe kujerar Sanatan
shiyyar Bauchi ta Arewa a karkashin jam'iyya mai ci ta APC.
DAGA ISYAKU.COM
Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Tags:
LABARI