Legit Hausa
A ranar Lahadi, wasu yan bindiga sun budewa motar sabon
gwamnan jihar Zamfara, Bello Matawalle, wuta yayinda yake hanyarsa na jajintawa
wadanda suka rasa yan uwansu a wani hari da aka kai karamar hukumar Gusau,
Premium Times ta bada rahoto. Masu Idanuwan shaida sun bayyana cewa an budewa
motar gwamnan wuta ne da yammacin Lahadi a hanyar garin Lilo.
Majiya ya bayyana cewa Yayinda suka kai harin, yan bindigan
sun yi amfani da damar tsayin ciyayi inda suka bude masa wuta. Ya kara da cewa
zuwa yanzu ba'a san yawan wadanda aka rasa ko suka jikkata ba, saboda masu
tsaron gwamnan sun yi batakashi da yan bindigan.
A rahoton da muka kawo da saifyar yau, mai magana da yawun
Sabon gwamnan jahar Zamfara, Bello Matawalle ya bayyaa cewa gwamnan ya
jagoranci ayarin jami’an rundunonin tsaro inda suka fantsama cikin dazukan
kauyen Wonaka dake garin Gusau da nufin farautar miyagun yan bindiga da suka
addabi al’ummar yankin.
Kaakakin, Yusuf Idris ya bayyana haka cikin wata sanarwa
daya fitar a ranar Lahadi, 2 ga watan Yuni, inda yace gwamnan ya samu rakiyar
mataimakin gwamnan jahar, Mahadi Aliyu Gusau, da sauran kwamandojin rundunar
tsaro, inda suka fatattaki yan bindigan.
A ranar Asabar, Akalla mutane 8 sun rasa rayukansu yayinda
18 suka jikkata harin da aka kai garin Lilo. Har ilau, jihar Zamfara da wasu
jihohi basu gushe suna fuskantar barazana daga wajen yan bindiga ba
DAGA ISYAKU.COM
Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi