Yanzu Yanzu: Shugabancin majalisar dattawa: Goje ya janye daga tseren ya mara wa Lawan baya


Legit Hausa

Bayan ganawa da Shugaban kasa Muhammadu Buhari a ranar Alhamis, 6 ga watan Yuni, Sanata Danjuma Goje ya janye daga tseren takarar kujerar Shugaban majalisar dattawa. A yanzu dai Goje ya jadadda goyon bayansa ga Shugaban masu rinjaye a majalisar dattawa, Sanata Ahmad Lawan domin darewa kujerar. 

Gwamnan jihar Kaduna, Mallam Nasir El-Rufai ne ya bayyana hakan bayan ganawr sirri da suka yi da Shugaban kasa Muhammadu Buhari a fadar Shugaban kasa da ke Abuja. Gwamna El-Rufai ya kasace tare da Sanata awan, Sanata Goje, da kuma babban mai ba Shugaban kasa shawara akan harkokin majalisar dokoki, Sanata Ita Enang a yayinda yake jawabi ga manema labarai na fadar Shugaban kasa. 

Yan majalisar dokoki kasar za su gudar da zabe domin maye gurbin Shugaban majalisar dattawa Bukola Saraki da wani a ranar 11 ga watan Yuni. Tun da fari dai shugabancin jam’iyyar All Progressives Congress (APC) sun nuna goyon bayansu ga Lawan a matsayin wanda suke so ya zama Shugaban majalisar dattawan.
 

DAGA ISYAKU.COM

Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN

 Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN