Legit Hausa
Akwai alamu masu karfi da ke nuna cewa rikici tsakanin
gwamnan jihar Kano Abdullahi Ganduje da Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II ya zo
karshe biyo bayan wata matsaya da aka cimma a daren ranar Juma’a a Abuja.
Da farko dai a ranar Juma’a Legit.ng ta rahoto cewa Shugaban
kasa Muhammadu Buhari ya shiga lamarin, biyo bayan kiran da aka yi kan ya sanya
baki da kuma yawan kira daga dattawan arewa yayinda rikici tsakanin gwamnan da
sarkin ke kara daga hakula a jihar.
Sanya bakin Shugaban kasa a lamarin na zuwa ne kwana daya
kafin wa’adin da gwamnatin jihar ta dibar ma sarkin akan yayi bayani game da
kudaden masarautar.
A taron sulhun da aka gudanar a daren ranar Juma’a a Abuja,
gwamnan da sarkin sun amince sun janye takobinsu don ra’ayin Kao da kuma rage
fargaba domin guje ma karya doka da oda.
Koda dai har yanzu babu cikakken bayani kan abunda ganawar
ta kunsa, wata majiya abun dogaro ta bayyana cewa Shugaban kungiyar gwamnonin
Najeriya kuma gwamnan jihar Ekiti, Kayode Fayemi ne ya jagoranci ganawar wacce
ta samu halartan yan tsirarun manyan mutane.
DAGA ISYAKU.COM
Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Tags:
LABARI