Legit Hausa
Shekara hudu bayan da Muhammadu Buhari yace matarshi bazata
rike ofishin Fes ledi ba, Aisha Buhari matar tasa, a ranar Alhamis ta bukaci da
a kirata da Fes ledi. Tun bayan da aka rantsar da Shugaba Buhari karo na farko
a matsayin shugaban kasar Najeria, ana kiran mai dakin nasa da matar shugaban
kasa.
Amma matar tashi Aisha ta ce daga yanzu mukamin nata ya koma
Fes ledi. Ta ce wannan zai magance rudanin da aka sanyawa matan gwamnoni game
da mukamin da suke dashi a jihohinsu. Ta ce "A lokacin da aka zabi mijina
karo na farko, ni na bukaci da a kirani da matar shugaban kasa."
"Amma na lura cewa hakan ya kawo rudani dangane da
yadda za a rinka kiran matan gwamnoni a jihohinsu." "Sabida haka ina
rokon ku gafara dangane da rudanin da na kawo, amma yanzu na zabi da a kirani
da Fes Ledi." a cewarta.
Wannan matsayar ta matar shugaban kasa ya sabawa alkawarin
da shugaba Buhari yayi a 2014 lokacin da yake takara, na cewa ba za ayi ofishin
Fes Ledi a gwamnatinsa ba. a wata hira da buhari yayi da jaridar weekly Trust a
cikin watan Satumba 2014, ya ce wannan ofishin na Fes Ledi babu shi a kundin
tsarin mulki kuma ya kamata a bari ministirin mata tayi aikin ta ba tare da
shiga huruminta ba. A lokacin ne Aisha Buhari ta bukaci da a kirata da matar
shugaban kasa.
Koma de wane suna ake yin amfani da shi, karfin ofishin
Aisha Buhari daya yake da na tsofaffin matan shugabannin kasa, a wani rahoto da
ICIR ta fitar. Bugu da kari, yanzu har sunan ana tsammani zai canza.
DAGA ISYAKU.COM
Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Tags:
LABARI