Legit Hausa
A ranar Lahad ne rahotanni suka bayyana cewar 'yan bindiga
sun bude wa tawagar gwamnan jihar Zamfara, Bello Matawalle, wuta a hanyarsa ta
zuwa yiwa jama'ar wani gari dake karkashin karamar hukumar Gusau jajen rashi da
asarar da suka yi sakamakon harin da 'yan bindiga suka kai musu. Amma gwamnan
ya ce jami'an tsaronsa ne suka fatattaki 'yan bindiga a wata mafakarsu.
A cewar wwani shaidar gani da ido, 'yan bindigar sun kai
harin ne a kan tawagar gwamnan yayinda yake kan hanyarsa ta kauyen Lilo domin
yiwa jaje da ta'aziyya. 'Yan bindigar sun yi amfani da yawan ababen hawa dake
bin hanyar tare da budewa tawagar gwamnan wuta.
Da gwamnatin jihar Zamfara ke musanta labarin kai wa gwamnan
hari a cikin wata sanarwa da ta fitar ranar Litinin, ta ce gwamnan da tawagar jami'an
tsaronsa ne suka kai wa 'yan bindigar hari sabanin labarin dake yawo a gari.
Yusuf Idris, kakakin gwamna, ya ce Matawalle ne ya jagoranci
jami'an tsaro wajen kai wa 'yan bindigar hari a maboyar su.Idris ya bayyana
cewar gwamnan na tare da mataimakinsa, Mahadi Aliyu Gusau, da kuma ragowar
shugabannin hukumomin tsaro na jihar Zamfara a lokacin da ya jagoranci kai wa
'yan bindigar hari.
A cewarsa, tawagar gwamnan ta samu nasarar fatattakar 'yan
bindigar daga sansaninsu a samamen da tawagar ta kai musu. "Duk da hakan,
gwuiwar gwamna ba tayi sanyi ba wajen wuce wa zuwa kauyen Lilo domin yi wa
jama'a jaje da ta'aziyya," a cewar jawabin.
Da yake karin haske a kan lamarin, gwana Matawalle ya ce;
"a matsayina na babban jami'in tsaron jiha, ya kamata na nuna wa ragowar
shugabannin hukomin tsaro da jama'a cewar kyakyawan misali ta hanyar nuna musu
yadda na damu na kawo karshen matsalar dake damun jama'a ta."
DAGA ISYAKU.COM
Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi