Wata sabuwa: APC ta yanke shawarar korar AbdulAziz Yari da Lawal Shuaibu daga jam’iyyar


Legit Hausa

Kwamitin bin diddigi wanda jam’iyyar All Progressives Congress (APC) ta nada domin gano matsalolin da jam’iyyar ta fada har yayi sanadiyar mummunar kaye da ta sha a zaben 2019 ta gabatar rahoton ta.

A cewar kwamitin tsarin yadda tsohon gwamnan jihar Zamfara, AbdulAziz Yari ya ja ragamar jam’iyyar na daya daga cikin babban dalilin da ya sa aka yi ta samun matsaloli a jam’iyyar da ya kai ga har ta sha kaye a zabukkan a aka yi a baya. Har ila yau, kwamitin ta ce ta samu labarin zagon kasa da mataimakin shugaban jam’iyyar APC na kasa reshen Arewa, Sanata Lawal Shuaibu ya rika yi wa jam’iyyar.

Sakataren APC reshen jihar Zamfara, Mohammed Bakyasuwa ne ya bayyana hakan yayinda yake zantawa da manema labarai a Abuja. "Ina so kowa ya kwana da sanin cewa tsakaninmu da bangaren Yari ba’a ga maciji yanzu saboda kuwa anja daaga. Yari ne shafaffen da ya saka jam’iyyarmu cikin kalubalen da muka tsinci kanmu a yanzu.

“Yanzu dai mun dauki matsaya guda cewa daga yau, mun kori AbdulAziz Yari da Sanata Lawali shu’aibu daga APC,. Kowa ya sani kuma wannan shine matsayar mu ‘yan jam’iyyar APC na Zamfara
 

DAGA ISYAKU.COM

Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN