Wani mutum da dansa sun yi mutuwar gaggawa a cikin wata rijiya a jihar Sokoto

Legit Hausa

Ba wannan ne karo na farko da aka taba yashe wata rijaya wadda tayi sanadiyyar mutuwar mutane hudu ba a Sokoto. Wannan ne karo na uku tun bayan da aka haka rijiyar kimanin shekara daya da wata biyu, amma wannan karon abun ya zo da hadari wanda ya bar al’ummar kauyen Baichi da ke garin Yabo a karamar hukumar Yabo ta jihar Sokoto cikin jimami.

Jaridar Daily Trust, ta gano cewa biyu daga cikin mamatan, uba da da, kwarrarun maginan rijiya ne. Lamarin ya faru ne da misalin karfe 9:00 na safe a lokacin da wani mazaunin kauyen da aka bayyana a matsayin malam Aliyu Shekare ya kira wani maginin rijiya da aka fi sani da Mai Zuma, don ya yashe masa rijiyarsa.

Mai Zuma, wanda maginin rijiya ne kuma mai saida zuma, ya taho tare da dansa, ya shiga rijiyar tare da injin na jan ruwa don ya fitar da laka daga cikin rijiyar wanda sanadiyyar hakan ya rasa iskan shaka ya mutu.

Daily Trust ta binciko cewa shima dan nasa ya mutu a cikin rijiyar a lokacin da yake kokarin ceto rayuwar mahaifin nasa. Wani mazaunin kauyen ya bayyana cewa “Mahaifin ya nemi taimako a lokacin da ya rasa iska ya jikata zai mutu, wanda hakan yasa dan nasa ya fada rijiyar don ya ceto mahaifin, amma shima sai ya rasa iska ya shake ya mutu.

Malam Aliyu Shekare ya bayyana cewa “Na tsorata na gigice bayan da nasamu wannan mummunan labari. Mai zuma ne ya gina mani wannan rijiyar. Kuma ba wannan ne karo na farko da na taba kiranshi ya yashe mani rijiar ba. Wannan ne karo na uku. Rijiyar na da tsawo taki takwas da rabi kuma duk sauran lokuttan Mai zuma ya yashe mani ita lafiya lau.”

Sauran mutum biyun da suka rayukansu sune Yahya Shanu wani malamin makaranta, yana da mata da yara biyu, dayan kuma shine Zaharadden Dodo, wanda ya kammala karatunsa a jami’ar Usmanu Danfodiyo dake Sokoto, kuma ya shirya tsaf zai tafi bautar kasa a jihar Osun washe garin ranar.

Yan kauyen sun kira masu kashe gobara wanda suka zo kuma tare da taimakon yan su, aka samu aka fitar da gawawwakin da misalin karfe 2:00 na rana. Wani daga cikin jami’an kashe gobara na sokoto ya tabbatar da cewa mamatan sun rasa iska ne sakamakon hayakin injin din jan ruwa da ake amfani dashi cikin rijiyar.

Mai garin kauyen na Baiche, Malam Muhammadu Dan Magaji ya ce wannan ne karo na farko da irin wannan ifila’i ya afku tun da ya hau mulki kimanin shekaru 16 da suka wuce. Mai garin ya kara da cewa sun mika lamarin ga ubangiji kuma zasu cigaba da mafani da rijiyar da aka rufe tun bayan afkuwar lamarin. Ya ce” Da rijiyar da ruwan ciki duk basu da illa.”
 

DAGA ISYAKU.COM

Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN

 Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN