Umarninka kawai muke jira - Majalisar dokokin tarayya ta sanar da Shugaba Buhari


Legit Hausa


Majalisar dattawa a jiya Alhamis, 13 ga watan Yuni tace a shirye take ta karbi duk wani umurni daga shugaban kasa Muhammadu Buhari. Majalisar dattawan ta tara wacce tayi zama na biyu a yanzu tace za ta tura wani sako zuwa ga Shugaban kasar ta ofishin babban sakataren gwamnatin tarayya.

Majalisar dattawan ta kuma ce za ta aika wani sako zuwa ga Shugaban kasar domin sanar masa cewa majalisar dattawa ta tara ta taru sannan cewa an zabi shugabannin ta, Ahmad Lawan a matsayin Shugaban majalisar dattawa, da kuma Ovie Omo-Agege a matsayin mataikain Shugaban majalisar dattawan.

Sanatocin sun kuma yanke shawarar aika wasikar taya murna ga kakakin majalisar wakilai Femi Gbajabiamila da mataimakin kakakin majalisar wakilai Ahmed Idris Wase a bisa nasara da suka yi da kuma sanar masu da zaben Lawan da Omo-Agege.
 

DAGA ISYAKU.COM

Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN