Legit
Hausa
Rundunar
sojin Najeriya ta ce ta kashe mutane 9 dake watsa labaran kungiyar Boko Haram,
wacce da ta rikide zuwa ISWAP, a kafafen sadarwa da dandalin sada zumunta.
Sagir Musa, darektan yada labarai da hulda da jama'a na rundunar sojin Najeriya,
ne ya sanar da hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar.
Ya ce
kashe 'yan kungiyar sadarwa na kungiyar Boko Haram ya tabbatar da cewar
rundunar soji ta gama gurgunta dukkan aiyukan kungiyar. Ya lisafa sunayen
mutane 9 da aka kashe kamar haka: Abu Hurayra al-Barnawi, Ali alGhalam
al-Kajiri, Abu Musab Muhammed Mustafa al-Maiduguri, Abu Abdullah Ali
al-Barnawi, da Abu Musa al-Camerooni. Ragowar sune; Ahmed al-Muhajir, Abu Ali
al-Bamawi, Abu Khubayb bin Ahmed al-Barnawi da Abu al-Qa'qa' al-Maiduguri.
"Kowa ya san kungiyar na amfani da
kafafen yada labarai domin yada farfaganda a kokarinta na kafa daular mulki
irin nata," a cewar sa. Kamfanin dillancin labarai na kasa (NAN) ya
rawaito cewar tun a shekarar 2009 kungiyar Boko Haram ta fara amfani da kafafen
sadarwa, musamman a dandalin sada zumunta, domin yada faifan bidiyo da lakcoci
domin jan hankalin matasa daga kasashen Najeriya, Nijar, Kamaru da Chadi su
shiga kungiyar.
NAN ta
kara da cewa kungiyar ta canja salo a shekarar 2014 ta hanyar bude shafuka da
dama a dandalin sada zumunta irin su 'Facebook' da Tuwita domin isar da sakonni
da kuma tuntubar jama'a.
DAGA ISYAKU.COM
Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi