Legit Hausa
Kamar yadda hukumar dakarun sojin kasa ta Najeriya ta
bayyana a ranar Asabar 15, ga watan Yunin 2019, an fara gudanar da shari'ar
wasu dakaru 14 a gaban kotun hukumar sojin mai tabbatar da da'a da kuma hukunci
a kan dakaru.
Jaridar Daily Nigerian ta ruwaito cewa, an fara gudanar da
wannan shari'a a kan dakarun soji 14 bayan sun shiga hannu da zargin aikata
miyagun laifuka na kisa, garkuwa da mutane da kuma wasu laifuka da suka sabawa
kundin tsarin mulkin kasa. Yayin fara zaman kotun a karo na farko da aka
kaddamar a birnin Fatakwal, babban jami'in soji mai kula da yankin na jihar
Ribas, Manjo Janar Jamil Sarham, ya ce ababen zargin sun kasance kanana da kuma
wasu manyan dakarun hukumar sojin kasa.
Manjo Janar Sarham ya ce kotun ta fara zamanta bisa ga
tanadin sashe na 131 cikin kundin tsarin hukumar dakarun sojin kasar nan domin
tabbatar da da'a da kuma kiyaye hukunce hukunce a tsakanin dakaru.
Jaridar Legit.ng ta fahimci cewa, laifukan wannan dakaru 14
sun hadar da kisa, garkuwa da mutane, kauracewa aiki, da kuma sabawa dokokin
hukumar dakarun soji ta kasar nan da babu shakka an yi tanadin hukuncin cikin
kundin tsari na hukumar da aka kaddamar tun a 2004. Babban jami'in na soji ya
kuma kara da cewa, wannan hukuncin da kotun tabbatar da da'ar dakaru za ta
zartar zai zamto izina da kuma jan kunne ga sauran dakaru masu mummunar manufa
ta sabawa doka.
DAGA ISYAKU.COM
Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi