Shugabancin majalisar dattawa: Sanatoci 61 sun lamuncewa Lawan – Kungiyar kamfen


Legit Hausa

Akalla zababbun sanatoci 61 ne suka shirya zabar Ahmed Lawan a matsayin shugaban majalisar dattawa, cewar kungiyar kamfen dinsa a ranar Asabar, 8 ga watan Yuni. Sakataren kungiyar, Barau Jibrin, ya karanto jerin sunayen ga yan jaridar a Transcorp Hilton Abuja. 

Mista Jibrin yace jerin sunayen ya hada 60 daga cikin zababben sanatocin APC 62 da kuma daya daga jam’iyyar Young Peoples Party (YPP). Yace a baya sunayen ya kai 64 amma daga bisani ya koma 62 sakamakon hukuncin kotu a kan jihar Zamfara. 

Ya nuna karfin gwiwar cewa sanatoci 61 za su zabi Mista Lawan. Jaridar Premium Times ta ruwaito cewa sanatoci 32 me kacal suka halarci taron. A baya shugaban kwamitin kamfen din, Yahaya Abdullahi, ya yi watsi da BATUN cewar Lawan na da izza kamar yadda wasu ke tunani.
 

DAGA ISYAKU.COM

Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN