Shugaba Buhari ya yi nadin sababbin mukamai a Najeriya


Legit Hausa

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya nada wasu sababbin Alkalai a kotun kolin kasar. Mun samu wannan labari ne a Ranar Lahadi 9 ga Watan Yuni, 2019, daga bakin Malam Garba Shehu. Garba Shehu wanda ya kasance mai magana da yawun bakin shugaban kasar, shi ya tabbatar da cewa shugaba Buhari ya nada wasu sababbin Alkalai a babban kotun Najeriya da ke Garin Abuja.

Shugaban kasar ya aikawa Alkalin Alkalan Najeriya na rikon kwarya takarda, inda yake sanar da shi game da wannan mataki da ya dauka. Hakan na nufin Alkalan kotun kolin sun kara yawa yanzu. Hadimin shugaban kasar ya bayyana cewa Muhammadu Buhari ya dauki wannan mataki na kara yawan Alkalan da ke kotun koli ne kamar yadda sashe na 230 na tsarin mulki ya ba sa cikakken iko. 

Malam Shehu wanda tun 2015 yake magana a madadin shugaban kasar ya ke cewa yanzu akwai Alkalai 21 a teburin babban kotun kasar, wanda wannan shi ne asalin abin da dokar Najeriya tayi tanadi. Mai magana da yawun bakin shugaba Buhari ya kara da cewa wannan mataki da gwamnatin Najeriya ta dauka yana cikin kokarin da ta ke yi na ganin shari’a na tafiya ba tare da kakkautawa ba.
Sai dai fadar shugaban kasar ba ta bayyana sunayen wadannan Alkalai da ta nada zuwa kotun kolin ba. A daidai wannan lokaci kuma shugaban kasar ya amince da murabus din tsohon CJN, Walter Onnoghen.
 

DAGA ISYAKU.COM

Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN