Sarkin Kano Sanusi ya yanto fursunoni da naira miliyan 5


Legit Hausa

Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II ya biya naia miliyan biyar na tarar da aka ci wasu fursunoni a gidajen yari na urmawa da Goron Dutse duk a cikin birnin Kano domin neman sakinsu. Da yake Magana a lokacin ziyarar da ya kai cikin wannan wata na Ramadana, Sarkin ya bukaci fursunonin da su duba zaman da suka yi a ggidan yari a matsayin nufi Allah sannan suyi amfani da hakan wajen koyon darasi. 

Ya shawarce su da suyi amfani da sauran ranakun da ya rage na Ramadana wajen neman gafarar Allah da kuma neman yardarsa domin ya shiga cikin lamarinsu. Ya kuma bukace su da su kasance masu kyawawan halayya domin guje ma duk wani aiki da zai sa su sake komawa gidan yari.

Mukaddashin Shugaban gidajen yari na jihar Kano, Aliyu Yahuza, ya bayyana ziyarar sarkin a matsayin abu da ke nuni ga cewa ya damu da talakawansa. Ya kara da cewa gidajen yari sun jajirce sosai wajen horar da fursunoni a fannin sana’o’i daban-daban.
 

DAGA ISYAKU.COM

Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews

 Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN