Legit Hausa
Tun kafin karewar zangon wa'adin ministocin da shugaban
kasa, Muhammadu Buhari, ya nada aka fara hasashen wadanne ministocin ne shugaba
Buhari zai cigaba da tafiya da su a zangon mulkinsa na biyu. Duk da shugaba
Buhari ya boye sirrin wadanda zai bawa mukamin minista a sabuwar gwamnatinsa,
wasu rahotanni sun bayyana jerin sunayen wasu tsofin ministoci 12 da ake
kyautata zaton zasu sake samun mukamin minista a zango na biyu na mulkin
Buhari.
Wani rahoto da jaridar 'The Cable' ta buga a ranar Lahadi,
ya ba bayyana wasu daga cikin dalilan da ake ganin sune silar dawowar wasu
ministoci 6 daga cikin goma sha biyun da aka wallafa. Jaridar ta ce wata
majiyarta a fadar shugaban kasa ce ta sanar da ita. Rotimi Amaechi, tsohon
ministan sufuri, ana tsammanin zai koma gwamnatin Buhari duk da saki-na-dafen
da ya yiwa jam'iyyar APC a jihar Ribas a takarar kujerar gwamna.
"Buhari zai mayar da Amaechi, hakan a bayyane take.
Abun zai yiwa Amaechi yawa idan aka ce Buhari ya ajiye shi. Waye ma wani jigo a
jam'iyyar APC daga yankin da ya yiwa Buhari wahala kamar Amaechi?," a
cewar majiyar. Suleiman Adamu, minista albarkatun ruwa, ana tsammanin shi ma
zai dawo. Yana daya daga cikin minstocin dake da kusanci da shugaba Buhari.
Tun farko ma ya samu minista ne ba don dalilin siyasa ba,
sai don alakarsa da shugaba Buhari, wacce ake zargin ta jini ce. Daga cikin
jerin minstocin akwai wadanda aka bayyana cewar zasu koma ne saboda suna da
kyakykyawar alaka ta musamman da shugaba Buhari.
Wadannan minitoci sune; Hadi Sirika, ministan harkokin
jiragen sama, Suleiman Hassan, ministan muhalli, Abdulrahman Dambazau,
minsistan harkokin cikin gida, da kuma Lai Mohammed, ministan yada labarai da
al'adu.
DAGA ISYAKU.COM
Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi