Legit Hausa
Tsohon shugaban jam’iyar All Progressives Congress APC Cif
John Odigie Oyegun ya sokawa Kwamarad Adams Oshiomole magana inda yake cewa
shugaban jam’iyar APC laifin wasu yake hangowa ba tare da yana duba nasa ba.
“ Kada Oshiomole ya rushe abinda wasu suka gina. Idan yana
bukatar a karantar dashi yadda zai tafiyar da jam’iyar ya zo ya nemi taimako, a
shirye nake da in taimaka mashi.” Inji tsohon shugaban Cif Oyegun yayi wannan
maganar ne a matsayin martini ga sakaraten hulda da jama’a na jam’iyar ta APC a
yanzu wato Mallam Lanre Issa Onilu wanda ya bayyana tsohon shugaban jam’iyar a
matsayin maras tsari wanda ya mayar da jam’iyarsu tamkar PDP.
Shi kuwa hadimin Cif Oyegun, mai kula hulda da jama’a Ray
Morphy a nashi zancen da ya fitar kan lamarin cewa yayi jagorancin maigidansa
daya ne tamkar da goma a wurin jam’iyar APC. Abinda takardar ta kunsa ya hada
da, rashin samun zaben fidda gwani mai inganci da haryanzu wasu yan takarar ke
kotu domin warwarware matsalarsu.
A karkashin jagorancin Oshiomole wanda ya kai kimanin
shekara daya kenan a yanzu inda da dama daga cikin yan jam’iyar APC ke ta sauya
sheka. “Kazalika, lokacin da Oyegun yayi jagoranci abin ba haka ya kasance ba.
An samu hadin kai da kuma zaman tsintsiya madaurinki daya tare da samu nasori
masu yawan gaske.” Inji hadimin Oyegun. Oshiomole a matsayinsa na babba bai iya
magance karamar matsala dake damun jam’iyar hakan ne ya janyo APC ta rasa
jihohi da dama duk da tarin karfin da take dashi
DAGA ISYAKU.COM
Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Tags:
LABARI