Legit Hausa
Shugaban jam’iyyar All Progressives Congress (APC), Adams
Oshiomhole, na a cikin tsaka mai wuya yayinda ake ta kulla-kullan ganin an
tsige shi daga kan kujerarsa. Jaridar Tribune ta ruwaito cewa akwai sabon
yunkuri da ake na ganin an fitar da shi daga sakatariyar jam’iyyar na kasa
yayinda yake shiri cika shekara guda akan kujerar shugabancin jam’iyyar.
Wata majiya ta jam’iyyar ta bayyana cewa gwamnoin APC sun
gabatar da wata bukata na son chanjin Shugaban jam’iyyar yayinda suka gana da
Shugaban kasa Muhammadu Buhari a mako da ya gabata. Gwamnan jihar Kebbi kuma
Shugaban gwamnonin jam’iyyar APC, Abubakar Atiku Baudu ya jagoranci
takwarorinsa zuwa wajeen ganawar.
An tattaro cewa gwamnonin APC a wajen ganawar da Buhari, sun
nuna damuwa kan rikici shugabanci da ke wakana a sakatariyar jam’iyyar na kasa
sannan suka roike shi kan ya sanya baki. Majiyar ta bayyana cewa da yiwuwa za a
gudanar da wani taro a tsakanin masu ruwa da tsaki na jam’iyyar a kasa da
kwamitin iyayen jam’iyya domin tattauna rikicin da ke tsakanin Oshiomhole da
mataimakinsa.
Majiyar ta kuma bayyana cewar gwamnonin na duba wanda zai
maye gurbin tsohon gwamnan na Edo a bayan Shugaban kasar. Sai dai an nemi jin
tab akin babban sakataren labaran jam’iyyar, Mallam Lanre Isa-Onilu, amma ba a
same shi ba. A nashi bangaren mataimakin kakakin jam’iyyar, Yakeen Nabena ya
bayyana a wayar tarho cewa bai da labarin kowani shiri na kiran taro asu ruwa
da tsaki na jam’iyyar.
DAGA ISYAKU.COM
Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Tags:
SIYASA