Rayuwa bayan mutuwa: Wata budurwa ta bayyana yadda ta dawo duniya bayan kwanaki da mutuwa


Legit Hausa

Labarin wata mata 'yar Najeriya na ta yawo a shafukan yada zumunta na zamani, bayan da ta bayyana cewa ta mutu sannan kuma ta dawo duniya bayan wasu kwanaki. 

Mhiz Gold Abi, 'yar Najeriya ce da take zaune a Casablanca, birnin kasar Morocco, an bayar da rahoton cewa ta mutu, inda abokanan ta suka yi ta mamakin labarin. Wasu daga cikinsu sunyi ta jajen mutuwarta a shafukan sada zumunta. Bayan wasu 'yan kwanaki kuma sai ta hau shafinta na sada zumunta na Facebook ta bayyana cewa ta dawo duniya.

A matsayin ta na wacce ta mutu ta dawo, wacce ta ga lahira, ta bayyanawa abokanan ta na Facebook cewa lahira babu dadi ko kadan, inda ta rubuta cikin harshen turanci kamar haka "Heaven no easy oo." Sannan tayi alkawarin bayyana irin abubuwan da ta gano a lahira, da irin abubuwan da suka faru da ita lokacin da take lahira.

Abokanan ta wadanda suka maida mata martani a labarin da ta rubuta din, sun bayyana jin dadinsu da ta dawo, sannan kuma sun yiwa Allah godiya da ya bata dama a karo na biyu.
 

DAGA ISYAKU.COM

Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN